1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ingancin bayanai a kan amfani da guba a Siriya

September 3, 2013

Majalisar dokokin Faransa za ta tafka muhawa a kan hujjojin zargin yin amfani da makamai masu guba a Siriya.

https://p.dw.com/p/19aWW
French President Francois Hollande gives a press conference on May 16, 2013 at the Elysee Palace in Paris, a day after his first anniversary in office was marred by news that France had fallen back into recession amid plummeting economic indicators. The Socialist leader, who is the most unpopular post-War president according to opinion polls, had pledged to turn back double-digit unemployment in Europe's second-largest economy this year, but that now seems highly unlikely. AFP PHOTO / PATRICK KOVARIK (Photo credit should read PATRICK KOVARIK/AFP/Getty Images)
Hoto: P. Kovarik/AFP/Getty Images

Gwamnatin Faransa ta mikawa majalisar dokokin kasar bayanai dangane da zargin Siriya da kaddamar da hare hare da makamai masu guba. A cewar rahoton na wannan Litinin, gwamnatin shugaba Assad ce ta kai hare haren a watan jiya domin fatattakar 'yan tawayen da ke wajen Damascus, babban birnin kasar. A wanna Larabar ce (03.09.13), majalisar dokokin kasar ta Faransa za ta tafka muhawara a kan batun. A karkashin tsarin mulkin Faransa dai, shugaba Francois Hollande , baya bukatar amincewar majalisar dokoki gabanin kaddamar da hari, kuma shugaban, bai nuna wata alamar neman majalisar ta jefa kuri'a a kan batun ba.

Dama a makon jiya ne majalisar dokokin Birtaniya ta jefa kuri'ar yin watsi da batun daukar matakin soji a Siriya, a wani abin da ke zama gagarumar koma baya ce ga kawayenta na kasashen yammacin duniya..

Can a kasar Amirka kuwa, gwamnatin shugaba Obama ce ta mika batun rikicin na Siriya ga majalisar dokoki, domin shiga tsakani, amma kuma 'yan majalisar dokokin na dari-dari game da batun. Senata John McCain, ya bayyana cewar, idan har majalisar dokokin ta jefa kuri'ar yin watsi da daukar matakin soji a Siriya, to, kuwa hakan zai zubar da mutuncin Amirka:

Ya ce " Idan har majalisar dokoki za ta yi watsi da kudiri - irin wannan, bayan da shugaban kasa ya mikashi gareta, to, kuwa sakamakonsa zai kasance mai hatsarin gaske, domin kuwa mutuncin wannan kasar zai zube a idanun kawayenta da makiyanta baki daya."

Majalisar dokokin dai za ta jefa kuri'a ne bayan dawowarta daga hutu.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Abdourahamane Hassane