1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iraki: Kurdawa na zaben neman ballewa

Abdul-raheem Hassan
September 25, 2017

A yau ne Kuradawan Iraki ke kada kuri'a a zaben raba gardama da zai basu damar ballewa daga gwamnatin Iraki, zaben dai ba shi da tasiri na cimma samun 'yancin cin gashin kai a mastayin yankin Kurdawa zalla.

https://p.dw.com/p/2kfap
Irak Kurden stimmen über Unabhängigkeit ab
Kurdawan Iraki na son yancin gashin kansuHoto: Reuters/T. Al-Sudani

Kawo yanzu dai wannan zabe na ci gaba da haifar da fargabar ga makomar zaman lafiya a yankunan da suka sha fama da masu tada kayar bayan kungiyar IS. A nasu bangaren gwamnatin Turkiyya, ta dauki matakan soji na toshe kan iyakar ta da yankunan Kurdawan a yunkurin nuna rashin goyon bayan zaben neman ballewar. Wannan ya sa Firaiminstan Iraki Haider al-Abadi, ya yi kakkausar suka ga matakin Kurdawan na neman raba kasa.

"Ba za mu yi watsi da al'ummar Kuradawa ba, mun yi watsi da shirin samar da yanki mai wariya. Iraki za ta ci gaba da kasancewa ta al'ummar Iraki, ba za mu amincewa kowa ya taka doka ba."