1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran: An cafke masu hannu a harin juma'a da ta gabata

Abdul-raheem Hassan
June 10, 2017

Hukumomin kasar Iran, sun tabbatar da kame mutane bakwai da ake zargi da hannu wajen kai harin bam a majalisar dokokin da ke Tehran.

https://p.dw.com/p/2eSmC
Iran Angriff auf das Parlament in Teheran
Hoto: picture-alliance/abaca/Fars/Vahabzadeh

Tun da farko ranar Jum'a da ta gabata humomin tsaro sun kame mutane 41 da ake tunanin suna da hannu a tagwayen hare-haren da suka yi  sanadiyyar mutuwar mutane 17 a majalisar dokokin kasar. Jami'an 'yan sanda na Iran din, sun kuma gano motar da maharan suka yi amfani da ita wajen kai hare-haren biyu na ranar Laraba a tsakiyar birnin kasar. Tuni dai Kungiyar IS ta dau alhakin kai wannan mummunan harin.