1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran: Shugaba Rouhani ya yi tir da wani aikin majalisa

December 2, 2020

Bangaren zartaswar Iran ya yi tir da wani aikin da 'yan majalisar kasar suka gudanar da fadar shugaban kasa ke cewa zai nakasa kokarin da take yi na dawo da ci gaba.

https://p.dw.com/p/3m8vT
Iran Beginn des neuen Schuljahrs
Hoto: irna

Shugaba Hassan Rouhani na kasar Iran ya bayyana adawarsa da wani kudurin dokar da majalisar kasar ta amince da shi, inda zai dakatar da sa idon Majalisar Dinkin Duniya kan harkokin makamashin Uranium na kasar.

Ra'ayin shugaban na Iran ne cewa matakin majalisar dokokin kasar zai maida hannun agogo baya a kokarin da ake yi na dawo da yarjejeniyar Nukiliyar kasar da aka cimma a 2015.

Jayayya kan kudurin dokar wanda ya samo karfi bayan kisan wani gwanin kimiyyar Nukiliyar makon jiya a kasar na tabbatar da karfin adawa da ke tsakanin Shugaba Rouhani mai matsakaicin ra'ayi da kuma 'yan majalisar kasar mai tsaurin ra'ayi.

Iran din dai na kokari a yanzu na ganin yadda za a kwance mata takunkuman tattalin arziki da Amirka ta kakaba mata.