1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta caccaki Birtaniya kan Hezbollah

Abdul-raheem Hassan
March 2, 2019

Gwamnatin Iran ta caccaki matakin Birtaniya na sanya kungiyar Hezbollah cikin jerin kungiyoyin ta'addanci a duniya tare da yin watsi da yunkurin haramta rassan kungiyar.

https://p.dw.com/p/3EMIR
Libanon Hisbollah Hassan Nassrallah
Hoto: picture-alliance/dpa

Birtaniya ta ce a shirye ta ke ta haramta duk wata rassa na kungiyar Hezbollah da ke gudanar da ayyuka a sassa daban-daban a fadin duniya, matakin na zuwa ne bayan da gwamnatin Amirka ta ayyana kungiyar Hezbollah cikin kungiyoyin ta'addanci na duniya bisa tasirinta a yankin gabas ta tsakiya. Shekaru 37 da suka gabata ne dakarun juyin juya hali na kasar Iran suka girka kungiyar Hezbollah da ke taka rawa a yakin da kasar Siriya ke yi da kungiyar IS.