1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta cika sharuddan IAEA

July 20, 2014

Iran ta amince ta lalata wani tarin nukiliyar da ta inganta wanda ake gani shi ne mafi hatsari, domin mututnta yarjejeniyar da ta kulla da kasashen yamma wanda zai rage mata takunkumi

https://p.dw.com/p/1Cfr8
Atomgespräche in Wien Juli 2014
Hoto: picture alliance/HANS PUNZ/APA/picturedesk.com

Iran ta amince ta lalata ajiyanta na wani nau'in iskar Urainium din da ta inganta, a karkashin wata kwarya-kwaryar yarjejeniyar da ta kulla da kasashe shidda masu karfin tattalin arziki a bara, wadanda suka hada da kasashe biyar masu kujerun dindindin a Majalisar Dinkin Duniya da Jamus.

Kamfanin dillancin labaran Reuters ne ya samo wannan labarin daga rahoton da hukumar sanya ido kan makamashi nukiliyar Majalisar Dinkin Duniya wato IAEA kan fitar wata-wata.

Wannan rahoton na IAEA ya nuna cewa Iran ta cika duka sharuddan da yarjejeniyar na watanni shidda ta gindaya wanda da ma ake sa ran wa'adin ta zai kare a ranar 20 ga watan Yuli, amma kuma aka amince a kara, tare da kwaskware wasu abubuwa, bayan da suka gaza cimma yarjejeniyar karshe wanda zai kawo karshen kace-nace kan makashin nukiliyar tsakanin Iran din da takwarorinta na Yamma.

Mawallafiya: Pinado Abdu Waba
Edita: Usman Shehu Usman