1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta jaddada 'yancinta na shirin nukiliya

October 7, 2013

Ministan harkokin wajen Iran Mohammad Javad Zarif ya ce ƙasarsa na da 'yancin gudanar da shirinta na nukiliya a cikin ƙasar.

https://p.dw.com/p/19vqb
An Iranian technician works at the control room of the Isfahan Uranium Conversion Facilities (UCF), 420 kms south of Tehran, 03 February 2007. Iran opened the doors to its uranium conversion plant today in a bid to show its good intentions amid mounting international pressure for a halt its controversial nuclear programme. A delegation of Non-Aligned Movement (NAM) and Group of 77 representatives arrived at the facility in the central city of Isfahan together with foreign and Iranian journalists for a guided tour. AFP PHOTO/BEHROUZ MEHRI (Photo credit should read BEHROUZ MEHRI/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images

Mr. Zarif ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da ya yi a birnin Tehran da takwaransa na Switzerland Yves Rossier, inda ya sake jaddada cewar Iran na da dukkannin 'yanci na gudanar da shirin na makamshin nukiliya na zaman lafiya ba tare da an yi mata katsalandan ba.

Isra'ila da ƙasashen yammacin duniya dai na zargi Iran ɗin da amfani da shirin wajen ƙera makaman ƙare dangi sai dai Iran din ta nace shirin nata na zaman lafiya ne, hasalima ta ce shiri ne na samar da makashi. A tsakiyar makon gobe ne dai ake sa ran komawa kan taburin tattaunawa kan shirin na nukiliyar Iran tsakaninta da ƙasashen da suka hada da Birtaniya da Faransa da China da Rasha da Amirka da kuma Jamus.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Abdourahamane Hassane