1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jagoran Facebook ya nemi afuwa

Abdul-raheem Hassan
March 22, 2018

Mark Zuckerberg ya ce wajibi ne ya dau matakan inganta manhajar don kare bayanan masu amfani da shafukan Facebook daga masu kutse.

https://p.dw.com/p/2ukNT
Mark Zuckerberg Facebook
Hoto: Reuters/S. Lam

Jagoran kamfanin sada zumunta na Facebook, ya nemi afuwar mutane akalla miliyan 50 kan yadda kamfanin Cambridge Analytica ta yi, wa masu amfani da shafukan kutsen bayan don cimma manufofi irin na siyasa.

Yayin wata hira da talabijin na CNN bayan bankado satar bayanan da kamfanin Cambridge Analytica ya yi, Zuckerberg ya ce tabbas an ha'inci jama'a. Tun dai bayan aukuwar lamarin, hannayen jarin kamfanin Facebook ya fadi da kashi Takwas cikin dari.