1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jama'ar Jihar Taraba na cikin damuwa

August 27, 2013

Al'ummar Taraba da ke a yankin arewa maso gabashin Nageria na ci gaba da bayyana rashin jin daɗinsu dangane da halin da gwaman jihar Danbaba Suntai yake ciki.

https://p.dw.com/p/19Xcg
Auf dem Bild: Parteizentrale PDP (Partei an der Macht in Nigeria) in Abuja, Nigeria. Foto: Ubale Musa, Haussa / DW
Hoto: DW/U.Haussa

Masu yin nazari a kan harkokin yau da kullum a jihar Taraba sun soma hangen wata barazanar kan siyasar jihar, biyo bayan dawowar Gwamnan Danbaba Suntai. Abin da dai ya fito fili shi ne na bambancin addini da 'yan siyasa ke amfani da shi wajen raba kawunan jama'a kamar yadda ya fito fili a garin Jalingo bayan dawowar Gwamnan.

Ruɗani da kuma sanin rashin tabbas a kan dawowar gwamna

Ko shakka babu gwamnan wanda aka dawoda shi ya tarad da jihar cikin wani ruɗani sakamakon jagorancin da mataimakinsa Alhaji Garba Umar ke kai, wanda wasu ke cewar ba ya tafiya yadda aka soma da farko. Alhaji AD Usman mai nazarin al'amura a jihar wanda ya tabbatar mani da cewar dawowar gwamna Suntai na zaman barazana ga jihar da ke fama da rikice-rikicen siyasa da na addini shekaru da dama ya ara da cewar.

Wahlplakat von Dr. Bamanga Tukur, Präsident der PDP ,( Partei an der Macht in Nigeria) Foto: Ubale Musa, Haussa / DW
Hoto: DW/U.Haussa

Ya ce : ''Dangane da yadda aka dawo da gwamnan ba tare da ya sami lafiya ba , wannan wani abu ne da zai ƙara kawo cikas ga yunƙurin da ake yi, na sauke shi daga muƙamin abin da ya ce an yi amfani da wata manufa ta addini.''

Sa-in-sa tsakanin 'yan siyasar a kan wannan batu

Sai da fa yayin da Alhaji AD Usman yake wannan kira, tsohon sakataren gwamnatin jihar mai kuma yin biyayya ga gwamna Suntai Ambasada Emmanuel Njiwa cewa yayi babu batun bambancin addini a wannan tafiya. Ya ce : '' Kawai gwamna Ɗanbaba Suntai ya dawo gida ne domin ci gaba da mulkin jihar kamar yadda talakwan suka ɗoramasa nauyi.''

Description en:House of Representatives of Nigeria Date 16 September 2005, 11:13 Source The House of Representatives Author Shiraz Chakera ou are free: to share – to copy, distribute and transmit the work to remix – to adapt the work Under the following conditions: attribution – You must attribute the work in the manner specified by the author or licensor (but not in any way that suggests that they endorse you or your use of the work). share alike – If you alter, transform, or build upon this work, you may distribute the resulting work only under the same or similar license to this one.
Ginin majalisar dokokin NajeriyaHoto: cc-by-sa/Shiraz Chakera

Akwai dai buƙatar mayar da hankali domin zaman fahimta cikin lumana a yanki a daidai wannan lokaci da gwamnan wanda dawowar tasa kamar yadda rahotanni suka tabbatar, babu wani jami'in gwamnatin da yayi tozali da shi, baya ga wata ziyarar ma da gwamnan jihar Adamawa Murtala Nyako ya kawo jihar domin marabtan shi gwamna Suntai ɗin da ba ta yi nasara ba, inda kamar yadda aka tabbabtar cewar gwamna Nyako bai samu saduwa da makwabcin nasa ba.

Mawallafi : Muntaqa Ahiwa

Edita : Abdourahamane Hassane