1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus da Faransa sun gargadi Ukrain kan siyasar kasar

Kamaluddeen SaniFebruary 23, 2016

Ministan harkokin wajen tarayyar Jamus Frank Walter Steinmeier da takawaran sa na kasar Faransa Jean-Mark Ayrault sun bukaci kasar Ukrain da ta gaggauta magance matsalolin siyasar kasar.

https://p.dw.com/p/1I0Oe
Ukraine Steinmeier, Ayrault und Klimkin
Hoto: Getty images/AFP/S. Supinsky

Ministocin sun yi wannan tsokacin ne a yayin da suke wata ziyara a kasar a inda suka jaddada zage dantse ga hukumomin kasar domin kawo karshen yakin 'yan awaren da ke a gabashin kasar.

Dukkanin ministocin harkokin kasashen biyu dai, sun kuma bukaci mahukuntan kasar fara aiwatar da wasu sabbin manufofin sauye-sauye da suka hada da tsari na dokokin zabe da yancin na musamman ga yankuna gami da yaki da cin hanci da rashawa.

Ziyarar ministocin ta zone kwana daya tak bayan da wasu mutane masu tarin yawa sun gudanar da wata zanga-zanga a birnin Kiev domin yin kiran murabus ga makaraban gwamnati tare da kiran gudanar da sabbin zabubbuka.