1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Merkel ta sake fuskantar karkarwar jiki

Binta Aliyu Zurmi
July 10, 2019

Shugabar Gwamnatin Jamus Angela Merkel ta sake fuskantar matsalar zanzana ko karkarwar jiki a karo na uku a bainar jama'a yayin da ta ke ganawa da Firaministan kasar Finland Antti Rinne a wannan Laraba a birnin Berlin.

https://p.dw.com/p/3LsKC
Deutschland | Finnland | Angela Merkel | Antti Rinne
Hoto: Reuters/H. Hanschke

Saidai da take bayani a gaban 'yan jarida tare da Firaministan kasar ta Finland,  Merkel ta ce tana cikin koshin lafiya. Sai dai ta ce ana yi mata bincike kan wannan matsala tata.

A ranar 18 ga Yunin da ya gabata ne Merkel da ke shirin cika shekaru 65 a ranar Laraba mai zuwa, ta fara fuskantar a karon farko wannan larura ta karkarwar jiki a lokacin da ta karbi bakuncin Shugaban Kasar Ukrain Volodymyr Zelenskiy a birnin Berlin, kafin matsalar ta sake dawo mata a ranar 27 ga watan na Yuni lokacin wata ganawa da shugaban kasar Jamus Frank-Walter Steinmeier awoyi kalilan kafi tashi zuwa taron koli na G20 a kasar Japan.