1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jirgin kasa ya kashe mutane 33 a Kwango

Abdul-raheem Hassan
November 13, 2017

Hukumomin kula da sufurin jiragen kasa sun ce mutane da dama sun jikkata a yayin da jirgin ya kife a rami, jami'ai na zargin mutanen da suka kone kurmus da shiga jirgin ba tare da izini ba.

https://p.dw.com/p/2nVVE
Iran Zugunglück
Hoto: picture-alliance/AP Photo/Fars

Jirgin kasan ya fada wani rami ne a yayin da yake kokarin haura wani tudu a kan titin birnin Lubumbashi birnin na biyu mafi girma a kasar zuwa Luenana, inda jirgin ya dauko tankokin mai 13da suka fashe suka haddasa gobara nan take bayan subuce wa zuwa rami.

A baya ansha samun hatsarin jiragen kasa a yankin Luena, kungiyar agaji ta kasa da kasa Red Cross tace akalla mutane mutane sama da dari sun mutu yayin da wasu sama da mutane 160 suka jikkata a wani hatsarin jirgin kasa da ya kife a shekarar 2014.