1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

AFCON: Kamaru ta yi raga-raga da Burkina Faso

January 9, 2022

2-1: Wannan shi ne sakamakon nasarar da Kamaru ta samu a kan Burkina Faso a wasan farko na AFCON da shugaban FIFA Gianni Infantino da Shugaba Paul Biya na Kamaru suka halartai a filin wasa mai daukar mutum 60,000.

https://p.dw.com/p/45K3S
Fußball Africa Cup of Nations | Kamerun v Burkina Faso
Hoto: MOHAMED ABD EL GHANY/REUTERS

Kasar Kamaru mai masaukin baki a gasar cin kofin Afirka ta AFCON da aka bude a yammacin wannan Lahadi ta fara gasar da kafar dama. A fafatawar da suka yi tsakaninsu da Burkina Faso, Kamarun ta yi nasarar zura kwalla 2 a raga, a yayin da Burkina Faso ta yi kokarin zura wa kamaru kwallo guda 1. 

Tun da farko sai da aka dauki lokaci ana bikin bude gasar da ke zama mafi daukaka a harkar kwallon kafa a nahiyar Afirka kafin a amincewa kasashen biyu da ke a rukunin A su kece raini.

An jima kadan da misalin karfe 8pm agogon Najeriya kasar Cape Verde da Habasha da su ma ke cikin rukunin A za su barje gumi a tsakaninsu a wannan gasa ta AFCON.