1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamaru ta haye mataki na gaba na AFCON

Suleiman Babayo MAB
January 31, 2022

Gasar neman cin kofin Afirka da ke gudana a kasar Kamaru ta kai matkin kusa da na karhe, kuma mai masaukin baki tana cikin kasashen da suka tsallaka zuwa wannan rukunin inda za ta kara da Masar.

https://p.dw.com/p/46KCO
Africa Cup of Nations | Kamerun gegen Gambia
Dan wasan Gambiya Badamosi ya kalubalanci Nouhou Tolo da Michael Ngadeu-Ngadjui na KamaruHoto: CHARLY TRIBALLEAU/AFP/Getty Images

Masar da Senegal sun bi sahun Kamaru da Burkina Faso wajen tsallakawa zuwa wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin kwallon kafan Afirka da ke gudana a Kamaru. A ranakun Laraba (02.02.2022) da Alhamis (03.02.2022) ne za a gudanar da wadannan wasanni.

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona da ke kasar Spain ta ce dan wasa Adama Traore zai sake komawa kungiyar bisa aro daga kungiyar Wolverhampton da ke Ingila har zuwa karshen kakar wasannin da ke wakana, kuma akwai yuwuwar a samu matsaya kan komawa kungiyar ta Barcelona baki daya daga bisani.

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da ke Ingila ta ce dan wasanta Mason Greenwood ba zai buga wasa ba nan gaba sakamakon koken da 'yan sanda suka samu na zargin sa da cin zarafin wata. 'Yan sandan sun tabbatar da fara bincike kan lamarin na dan wasan Mason Greenwood dan shekaru 20 da haihuwa.

Australian Open Finale | Daniil Medvedev gegen Rafael Nadal
Daniil Medvedev ya fafata da Rafael NadalHoto: Andy Brownbill/AP/picture alliance

An kammala gasar tennis ta ostareliya

An kammala gasar wasan tennis na Ostareliya cikin wani yanayi na annashuwa da yammacin ranar Lahadi. Da ma dai jama'a sun zaci cewa wasan ba zai kayatar ba, bayan da mahukuntan kasar s ka tasa keyar tauraron wasan Novak Djokovic bisa zargin shi da karya dokokin da suka shafi annobar COVID-19. Amma gasar ta bana ta kafa tarihi iri-iri ta kuma kayatar da duniya.