1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamaru ta yi nasarar kubutar da mutanenta

Muntaqa AhiwaJanuary 19, 2015

Sojojin kasar ne suka kwato mutane 24 daga cikin 80 da kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da su a kan iyakar kasar da makwabciyar ta Najeriya a jiya Lahadi.

https://p.dw.com/p/1EMvI
Kamerun Amchide Polizei Spezial Soldaten Anti Boko Haram 07/2014
Hoto: Reinnier Kaze/AFP/Getty Images

Harin da Boko Haram din ta kaddamar kan kauyen Mabass, ya kasance hari mafi girma da ya kai ga garkuwa da jama'a a kasar, inda a ciki aka yi garkuwa da kananan yara.

Kamar dai yadda kakakin ma'aikatar tsaron kasar ta Kamaru, Kanal Didier Badjeck ya shaida wa manma labarai, sojojin na Kamaru sun yi nasarar kwato 'yan kasar ta su ne, sakamakon matsawa 'yan bindigan da ke kan hanyar su ta komawa cikin tungar su da ke a Najeriya.

Kungiyar Boko Haram dai ta kashe dubban mutane tare da garkuwa da daruruwan wasu a arewacin Najeriya.

Mawallafi: Muntaqa Ahiwa

edita: Usman Shehu Usman