1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kare fararen hula a birnin Goma

July 19, 2013

Majalisar Dinkin Duniya ta kuduri aniyar inganta matakan ba da kariya ga mazauna gabacin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo mai fama da rikici.

https://p.dw.com/p/19Ay0
Displaced Congolese flee on July 15, 2013 the area of Kanyarucinya through Munigi on the outskirts of Goma in the east of the Democratic Republic of the Congo. At least 130 people were killed, including 10 soldiers, in the deadliest clashes in months between troops and rebels in the restive eastern Democratic Republic of Congo, the government said on July 15. Fierce fighting broke out on July 14 outside the flashpoint city of Goma between the Congolese army and the M23 rebels, an armed group launched by Tutsi former soldiers who mutinied in April 2012. The clashes continued on July 15 between Congolese armed forces and M23 rebels, causing several thousands of people to flee. AFP PHOTO / PHIL MOORE (Photo credit should read PHIL MOORE/AFP/Getty Images)
Hoto: Phil Moore/AFP/Getty Images

A saboda haka ne Majalisar ta fara tura karin dakarun yaki da za su kare birnin Goma daga mayakan 'yan tawaye. Hakan dai na zuwa ne bayan da al'ummomin yankin suka gudanar da wata zanga-zanga inda suka zargi sojojin wanzar da zaman lafiya da rashin tabuka wani abin kirki don kare su.

Kawo yanzu dai dakarun Majalisar Dinkin Duniya a kasar ta Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo ba sa tsoma baki a rikicin da ake yi da 'yan tawaye, kuma suna kallo a wannan makon lokacin da mayakan kungiyar M23 suka kaddamar da sabon farmaki a kan dakarun gwamnati a kewayen birnin Goma dake zama birni mafi girma a gabacin kasar. Sai dai kakakin rundunar Majalisar Dinkin Duniya a Kongo MONUSCO, wato Martin Nesirky ya ce rundunar tana cikin damara kuma a shirye take ta tsoma baki idan fadan ya zama barazana ga fararen hula musamman a birnin na Goma.

Kare birnin Goma shi ne muhimmi

A cikin watan Maris ne Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya ya amince da tura karin dakaru da ya ba su ikon shiga yaki gadan-gadan musamman da 'yan tawaye. Ko shin wannan mataki da Majalisar ta dauka yanzu zai dawo da martabarta a idanun fararen hular Kongo da suka jima suna zarginta da rashin wani katabus? A hirarsu da DW kwamandan rundunar MONUSCO kuma dan kasar Brazil Carlos Alberto dos Santos Cruz ya ce abin da suka fi ba wa fifiko shi ne kare fararen hula.

epa03676473 (FILE) A file picture dated 28 March 2007 shows the MINUSTAH troops chief, Brazilian General Carlos Alberto Dos Santos Cruz, during a visit to Citi Soleil neighborhood in Port au Prince, Haiti. Dos Santos Cruz will lead the Monusco Mission of The United Nations in Congo. The 60-year old general is appointed to command almost 20,000 soldiers from 20 countries in the Democratic Republic of the Congo with the task of targeting rebels in the east of the country. EPA/DAVID FERNANDEZ +++(c) dpa - Bildfunk+++
General Carlos Alberto dos Santos Cruz, kwamandan rundunar MONUSCOHoto: picture-alliance/dpa

"Kongo na fama da matsaloli da kungiyoyi da yawa na masu daukar makamai da suka addabi gabacin kasar. Saboda haka jama'a suka damu da a magance matsalolin. Akwai matsalolin rashin ababan more rayuwa da na hanyoyin sadarwa. Ina da tabbacin cewa za a iya magance matsalolin, amma ba a cikin dare daya ba."

Rundunar ta MONUSCO ta kunshi sojoji da ma'aikata fararen hula fiye da dubu 22 kuma ita ce wata tawaga mafi girma da Majalisar Dinkin Duniya ta taba samarwa. Yanzu haka kimanin kashi biyu bisa uku na sojojin rundunar suna a gabacin Kongo inda suke ba da kariya a ciki da wajen Goma da kuma sansanonin 'yan gudun hijira. Rundunar tana kuma horas da sojojin Kongo a game da batuuwan da suka shafi kare 'yancin dan Adam da yadda ake aiki a wuraren da ake fama da rigingimu kamar na kan iyakar Kongon da kasashe makwabtanta, inji kwamandan rundunar Carlos dos Santos Cruz.

"Matsalar gabacin Kongo ta shafi yankin gaba daya kasancewa rikici ne a kan iyakoki, saboda haka kamata yayi a warware matsalar a siyasance. A nan kuwa sojoji za su iya taimakawa. Dole ne dukkan masu hannu cikin rikicin su zage damtse idan ba haka ba haka ba zai yi wuya a gano bakin warware rikicin."

A Congolese army soldier walks through the bush, back from an attack position north-west of Munigi, overlooking the front-line, in the east of the Democratic Republic of the Congo on July 15, 2013. Fighting broke out yesterday between M23 rebels and the national army, and continued today, with heavy artillery fire north-west of Munigi and the army claiming to have taken ground. AFP PHOTO/PHIL MOORE (Photo credit should read PHIL MOORE/AFP/Getty Images)
Hoto: Phil Moore/AFP/Getty Images

Ko da yake fadan da ake a kewayen birnin Goma ya lafa a ranar Alhamis, amma an ci gaba da zanga-zangar yin tir da Majalisar Dinkin Duniya.

A halin da ake ciki babban sakataren Majalisar ta Dinkin Duniya Ban Ki Moon ya nuna matukar damuwarsa ga sabon rikicin na birnin Goma da kewayen arewacin Kivu, sannan yayi kira ga dukkan sassan da abin ya shafa da su nuna halin ya kamata kana su guji yin abubuwan da za su kara tsananta rikici tare da jefa rayuwar jama'a cikin mawuyacin hali.

Mawallafa: Marta Barroso / Mohammad Nasiru Awal
Edita: Halima Balaraba Abbas