1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zimbabuwe ta dauki alwashin inganta alaka da China

Zulaiha Abubakar MNA
April 3, 2018

Shugaban kasar Zimbabuwe Emmerson Mnangagwa ya gode wa shugaban kasar China Xi Jinping kan irin gudummawar siyasar da yake ba kasarsa tare da daukar alwashin inganta alaka tsakanin kasashen biyu.

https://p.dw.com/p/2vPuY
Simbabwe Emmerson Mnangagwa Rede in Harare
Hoto: Reuters/P. Bulawayo

Shugaba Mnangagwa ya bayyana haka ne a wannan Talata yayin da yake ganawa da shugaban kasar China Xi Jinping a wata ziyara irinta ta farko da ya kai China, bayan darewarsa kujerar shugabancin Zimbabuwe.

A baya dai tsohon shugaban kasar Robert Mugabe ya kyautata alakar kasashen biyu duk kuwa da cewar an zarge shi da yada cin hanci a lokacin mulkinsa.

Tun a baya China ta cigaba da alaka da Zimbabuwe duk kuwa da janye alaka da kasar da kasashen yammacin Turai suka yi bisa rahotannin keta haddin dan Adam a lokacin mulkin Robert Mugabe.