1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashen duniya na ci gaba da agazawa Philippines

November 13, 2013

Kuwait ta amsa kiran da Majalisar Dinkin Duniya ta yi na agaji ga al'ummar Philippines, bayan bala'in da ya afka wa kasar.

https://p.dw.com/p/1AHEO
epa03946220 A handout picture made available by the Philippine Red Cross (PRC), shows volunteers helping in packing relief goods for typhoon-affected families in Manila, Philippines, 12 November 2013. International aid poured in for the Philippines as authorities stepped up efforts to reach survivors driven to looting after one of the world's strongest typhoons devastated their towns. A tropical depression brought heavy rains over the central and eastern Philippines, where provinces badly hit by Haiyan are located, raising concerns that relief operations would be hampered. EPA/PHILIPPINE RED CROSS HANDOUT EDITORIAL USE ONLY/NO SALES
Hoto: picture-alliance/dpa

Sarkin daular Kuwait Sheikh Sabah al-Ahmad Al-Sabah, ya bayar da umarnin tura agajin gaggawa da ya kai na kudi dalar Amirka miliyan 10 zuwa ga dubbannin jama'a da mahaukaciyar guguwar nan ta Hyan ta yi wa ta'adi a kasar Philippines, inda kuma ake fargabar mutuwar mutane da dama. Kamfanin dillancin labaran kasar Kuwait ya ambaci ministan kula da harkokin majalisar ministoci a kasar, Sheikh Mohammad Abdullah Al-Sabah yana cewar, Ba-Saraken ya yi hakanne domin agazawa dimbin jama'ar da suka shiga cikin ukuba. Dama dai Majalisar Dinkin Duniya ta kaddamar da asusun neman agaji na fiye da dala miliyan 300 domin tallafa wa mutanen da matsalar ta rutsa dasu. Babbar jami'ar kula da harkokin agaji na Majalisar Dinkin Duniya Valerie Amos, ta sanar - a birnin Manila cewar, suna bukatar kudin ne domin abinci da magunguna da samar da matsugunai ga jama'a.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Pinado Abdu Waba