1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Keita ya lashe zaben Mali da gagarumin rinjaye

August 15, 2013

Hukumomin zabe a kasar ta Mali sun ce Ibrahim Boubacar Keita ya samu kimanin kashi 78 cikin 100 na yawan kuri'un da aka kada a zagaye na biyu na zaben.

https://p.dw.com/p/19QZG
Presidential candidate Ibrahim Boubacar Keita speaks in front of a picture of himself during a news conference Bamako, Mali, August 4, 2013. The candidate of Mali's largest political party, who came third in the first round of the country's presidential election, broke ranks with his own party on Saturday and said he will back former prime minister Keita in a run-off. REUTERS/Joe Penney (MALI - Tags: ELECTION POLITICS)
Hoto: Reuters

Sakamakon da aka bayar a hukumance a wannan Alhamis na zaben shugaban kasar Mali zagaye na biyu ya nuna cewa shugaban da aka zaba Ibrahim Boubacar Keita ya lashe zaben da gagarumin rinjaye. Hukumomin zabe a kasar ta Mali sun ce Keita ya samu fiye da kashi 77 cikin 100 na yawan kuri'un da aka kada yayin da abokin hamaiyarsa Souma'ila Cisse ya samu kimanin kashi 22 cikin 100. Sai dai yawan wadanda suka kada kuri'a a zaben na ranar Lahadi bai kai wadanda suka sauke wannan nauyi a zagayen farko na zaben ba. A hukumance kashi 46 cikin 100 na wadanda suka cancanci kada kuri'a a kasar suka sauke wannan nauyi. Ana sa rai a wata mai zuwa za a rantsar da Keita a mukamin shugaban kasa, watanni 18 bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa tsohuwar gwamnatin demokradiyyar kasar.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu