1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kenya za ta ci gaba da kyale dakarunta a Somaliya

October 1, 2013

Shugaban Kenya ya sha alwashin ci gaba da tallafa wa gwamnatin Somaliya wajen yaki da al-Shabab.

https://p.dw.com/p/19sJJ
Armed Kenyan policemen take cover outside the Westgate mall in Nairobi on September 23, 2013. Kenyan troops were locked in a fierce firefight with Somali militants inside an upmarket Nairobi shopping mall on September 22 in a final push to end a siege that has left at least 69 dead and 200 wounded with an unknown number of hostages still being held. Somalia's Al Qaeda-inspired Shebab rebels said the carnage at the part Israeli-owned complex mall was in retaliation for Kenya's military intervention in Somalia, where African Union troops are battling the Islamists. AFP PHOTO / SIMON MAINA (Photo credit should read SIMON MAINA/AFP/Getty Images)
Hoto: SIMON MAINA/AFP/Getty Images

Shugaba Uhuru Kenyatta na kasar Kenya, ya bayyana cewar, kasar, za ta ci gaba da kyale dakarunta da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Somaliya domin taimakawa gwamnatin kasar ta Somaliya wadda ke tangal-tangal ci gaba da tinkarar kungiyar al-Shabab, wadda ta kai hari a kan cibiyar kasuwanci ta birnin Nairobi a ranar 21 ga watan Satumban da ya gabata. Kungiyar ta ce harin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar a kalla mutane 67, martani ne ga dakarun da kasar ta Kenya ta tura a Somaliya da ke makwabtaka da kasar tun a shekara ta 20011. Hakanan kungiyar ta yi wa Kenya kashedin cewar, za ta ci gaba da fuskantar makamancin harin da ta kai a cibiyar kasuwancin - muddin dai ba ta janye dakarunta daga kasar ba. A lokacin wani taron addu'a a wannan Talatar (01. 01. 13), shugaba Kenyata ya ce zai samar da wata hukumar bincike, wadda za ta tantance wuraren da aka samu kuskure ta fuskar tsaro domin kiyaye gaba.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Umaru Aliyu