1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Koriya ta Arewa da ta Kudu za su tattauna

Yusuf Bala Nayaya
January 5, 2018

Koriya ta Arewa da takwararta Koriya ta Kudu sun amince a hukumance da fara tattaunawa a mako mai zuwa kan hadin kai da za a samu a shirin wasannin Olympic lokacin hunturu da za a yi a Koriya ta Kudu.

https://p.dw.com/p/2qNDP
Donald Trump und Kim Jong Un TV Bild in Seoul
Hoto: picture alliance/AP Photo/A. Young-joon

Mahukuntan na birnin Seoul sun bayyana haka ne sa'oi bayan da Amirka ta bayyana cewa za ta tsagaita shirin atisaye da sojan kasarta tare da takwarorinsu na Koriya ta Kudun ke yi har sai angama wasannin na Olympic.

A ranar Jumma'an nan kuma Koriya ta Arewa ta tura da sako zuwa ga takwarar tata Koriya ta Kudu inda ta ce za ta amince da shirin tattaunawar na garin Panmunjom da ke kan iyakar kasashen biyu a ranar Talata don tattaunawa kan shirin na gasar Olympic da ma tattauna alakar kasashen biyu.

Ana dai kallon duk wani shiri na tattaunawa tsakanin kasashen biyu a matsayin abu mai muhimmanci a kokari na samar da zaman lafiya tsakanin kasashen, sai dai wasu masharhanta na ganin cewa Koriya ta Arewa na son amfani da damar wajen raba kan mahukunatan na Seoul da na Washington, haka nan kuma ta rage matsin lamba da kasar ke samu tsakanin kasa da kasa, da ma neman sassauci kan tarin takunkumi da aka kakaba wa kasar ta Koriya ta Arewa.