1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Koriya ta Arewa ta yi sabbin gwaje gwajen makaman nukiliya.

February 12, 2013

Ƙasashen duniya na ci- gaba da mayar da martani da kakkausar ga Koriya ta Arewa,dangane da abin da suka kira karya dokokin ƙasa da ƙasa.

https://p.dw.com/p/17cq7
A passenger walks past a television report on North Korea's nuclear test at a railway station in Seoul February 12, 2013. North Korea conducted a nuclear test on Tuesday, South Korea's defence ministry said, after seismic activity measuring 4.9 magnitude was registered by the U.S. Geological Survey. The epicentre of the seismic activity, which was only one km below the Earth's surface, was close to the North's known nuclear test site. REUTERS/Kim Hong-Ji (SOUTH KOREA - Tags: POLITICS)
Hoto: Reuters

Babban sakataran Majalisar Ɗinkin Duniya Ban Ki Moon a cikin wata sanarwa da kakakinsa ya baiyana, ya ce wannan gwaje gwaje sun saɓama dokokin kwamitin sulhu na MDD.Shugaba Barack Obama na Amirka ya sanar da cewar yunƙurin tsokana ce, kana kuma barazana ga Amirka da kuma yankin baki ɗaya.

Ministan harkokin waje na ƙasar Rasha Sergei Lavrov ya ce sun gargaɗi Koriya da ta yi watsi da shirinta tare da mutunta dokokin MDD.Yayin da ƙasar China ta yi kira ga ƙawarta da ta bi ummarnin dokokin ƙasa da ƙasa tare da gayatar jakadin Koriya ta Arewa domin ba da baiyani.Nan gaba kuma a ka shirya kwamitin sulhu na MDD zai yi wani zama na musammun domin ɗaukar matakan ladabtarwa a kan Koriya ta Arewa, wacce tuni ta sanar da cewar baza ta fasa yin gwaje gwajen ba.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammed Awal Balarabe