1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta tuhumi tsohon shugaban Chadi

July 2, 2013

Ana tuhumar Hissene Habre da aikata laifukan yaki da kisan ƙare dangi da kuma azabtarwa a kan jama'a a lokacin muklinsa Tsakanin shekarun 1982 zuwa 1990 a Chadi.

https://p.dw.com/p/190yO
Das undatierte Archivbild zeigt den Ex-Präsidenten des Tschad, Hissene Habre. Menschenrechtler in Afrika wollen Habre, den Ex-Machthaber des Sahelstaates Tschad, vor Gericht bringen. «Habre ist Afrikas Pinochet», sagte in Dakar Reed Brody von der internationalen Menschenrechtsorganisation Human Rights Watch. Während Habres Regierungszeit (1982-1990) sollen nach Angaben einer Wahrheitskommission 40 000 Menschen aus politischen Gründen ermordet und 200 000 gefoltert worden sein. Habre (57) lebt im Exil in der senegalesischen Hauptstadt Dakar. dpa (zu dpa 0007 vom 28.01.2000)
Hoto: picture-alliance/dpa

Da yake yinn tsokaci a kan tuhumar lauyan da ke kare tsohon shugaban Maitre Diouf ya ce :'' Habre na fuskantar wani al' amari ne, na sace shi da aka yi, kana aka yi garkuwa da shi, wanda kuma ya ce muke ɗora alhakin haka a kan wasu sojojin.''

Hissene Habre ɗan shekaru 71 a duniya na zaune a ƙasar ta Senegal tun a shekara ta 1990 lokacin da gwamnatinsa ta faɗi. Nan gaba ne dai kotun ta musammun da aka kafa za ta yi masa shari'a, a kan zargin da ake yi masa na aikAta kisa a kan mutane kusan dubu 40 waɗanda wasunsu suka mutu a gidajen kurkuku.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe