1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar AU ta bukaci Trump ya nemi gafara

Abdul-raheem Hassan
January 13, 2018

Kungiyar Tarayyar Afirka AU ta yi Allah wadai da kalaman wulakanci da aka zargin shugaba Donald Trump ya aikatawa a kan kasashen Afirka da kasar Haithi hada da kasar El Salvador.

https://p.dw.com/p/2qn7o
Versammlung der Afrikanischen Union in Addis Ababa
Hoto: picture alliance/AA/M. Wondimu Hailu

An dai zargi shugaba Trump da subul dan baka ne a yayin ganawarsa da masana harkokin shari'a domin tattauna yiwuwar sake kwaskwarima kan tsarin 'yan ci rani da ke cikin Amirka.

Duk da cewa fadar shugaban Amirka sun nesanta Trump da amfani da kalamai marasa dadi, amma kungiyar AU ta bukaci shugaban da ya nemi gafarar kasashen Afirka da Haithi da kuma El Salvador da ya tozartasu.