1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar Taliban ta sako mutane 235

Ramatu Garba Baba
August 8, 2017

Kungiyar Taliban a Afganistan ta sako wasu mutane 235 da ta yi garkuwa da su a wani kauye mai suna Mirzawalang.

https://p.dw.com/p/2hu5q
Pakistan Taliban-Überfall auf Schule in Peshawar 16.12.2014
Hoto: Reuters/K. Parvez

Kungiyar Taliban a Afganistan ta sako wasu mutane 235 da ta yi garkuwa da su a wani kauye mai suna Mirzawalang da ke yankin arewacin kasar. Mayakan na Taliban sun yi garkuwa da wadanan mutanen ne a  wani farmaki da suka kai kauyen a can baya inda suka hallaka fararren hula fiye da hamsin.

Akwai mata da kananan yara a cikin wadanda aka sakon. Kakakin gwamnan yankin Zabihullah Amani ya ce an cimma matsaya da sa bakin dattijan kauyen da ma bangaren wakilan yankin, ya kuma kara da cewa akwai wasu da ba za a iya tantance yawansu ba da mayakan ke ci gaba da yin garkuwa da su.