A shirin na wannan lokaci, zaku ji cewa a Jamhuriyar Nijar wata sabuwar takaddama ta barke tsakanin 'yan wasan kwallon kafar kasar MENA Natioanl da hukumomin wasannin kwallon kafar kasar, game da kudaden alawus-alawus din da suke bin gwamanti har na tsahon shekaru biyu. Hukumomin dai sun gayyaci 'yan wasan a baya-bayan nan, sai dai wasu da dama sun ki su amsa gayyatar.