1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD: An karrama Likita a Sudan ta Kudu

Yusuf Bala Nayaya
September 25, 2018

Evan Atar Adaha dan shekaru 52 da ke kula da asibiti daya tilo a yankin arewa maso gabashi na yankin Maban ya rika daukar kasadar siyar da rai don tallafar al'umma.

https://p.dw.com/p/35RFj
Tuberkolose
Marasa lafiya a wani asibitin kudancin DafurHoto: picture-alliance/dpa

Wani likita dan kasar Sudan ta Kudu ya samu lambar yabo ta hukuma da ke kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya bayan da ya kwashe kusan shekaru 20 yana taimakon mutane da ke zama marasa lafiya a kasarsa da ke yankin gabashin Afirka wacce ke fama da tashe-tashen hankula. An bayyana wannan likita ne da samun wannan gagarumar girmamawa bayan da ya kula dubban marasa lafiya wadanda ke gujewa tashe-tashen hankula da ma gudun tsira da rai.

Evan Atar Adaha dan shekaru 52 da ke kula da asibiti daya tilo a yankin arewa maso gabashi na yankin Maban ya samu lambar yabon da ake kira Nansen Refugee Award a Turance saboda yadda ya sadaukar da rai wajen taimakon rayukan al'umma duk da cewar a lokuta da dama yana daukar kasada da ka iya sanadi na rasa ransa a cewar MDD.