1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Madugun adawan Zimbabuwe ya rasu

Ramatu Garba Baba
February 15, 2018

Al'ummar kasar Zimbabuwe na ci gaba da jimamin mutuwar madugun adawa kuma tsohon Firaiministan kasar Morgan Tsvangirai bayan da ya sha fama da cutar kansar hanta.

https://p.dw.com/p/2simk
Simbabwe Morgan Tsvangarai verhaftet
Hoto: AP

Tsvangarai ya rasu a wani asibiti da ke a Afrika ta Kudu a wannan  Laraba. Elias Mudzuri daya daga cikin jagorin jam'iyyar adawa ta MDC ne ya sanar da mutuwar.

Tsvangarai shi ne mutumin da ya kafa jam'iyyar MDC a shekarar 2000, ya kuma kwashi shekaru da dama ya na adawa da Robert Mugabe tsohon shugaban kasar ta Zimbabuwe. Madugun adawan ya sha jagoranta gangami don kalubalantar mulkin Mugabe na wancan lokacin lamarin da ya kai shi ga zaman gidan kurkuku a sau da yawa. Marigayin ya rasu ya na da shekaru sittin da biyar.