1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majagin garin London ya goyi bayan ficewar kasar daga EU

Kamaluddeen SaniFebruary 22, 2016

A ranar Lahadin nan ce magajin garin birnin London Boris Johnson ya bayyana cewar a shirye yake wajen ganin ya goyi bayan ficewar Britaniya daga cikin kungiyar EU.

https://p.dw.com/p/1Hzbz
London Bürgermeister Boris Johnson
Hoto: picture-alliance/Zuma/S. Lock

Matakin na magajin garin London din ya zone a matsayin wani babban koma baya ga Firiminista David Cameron wanda kwana daya tak kafin magajin garin ya furta kalaman bayan da Firiministan ya ce za a gudanar da kuri'ar raba gardama a ranar 23 ga watan Yuni da ke tafe.

Boris Johson ya kara da cewar,

"Na yanke hukuncin ne bayan nisan tunani da kaiwa da komowa, kuma abu na karshe da zan iya yi shi ne na saba da muradin David Cameron ko kuma gwamnatin, ina goyan bayan ficewa daga kungiyar ko da kuwa me za a ce."