1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Dinkin Duniya ta amince da ɗaukar matakin soja a Mali

December 21, 2012

Bayan kai ruwa rana da aka sha yi,a ƙarshe Komitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kaɗa ƙuri'ar amincewa da tura dakaru a arewacin Mali.

https://p.dw.com/p/177Iu
The United Nations Security Council meets at the United Nations in New York to discuss the ongoing violence in Syria April 21, 2012. The U.N. Security Council unanimously adopted a resolution on Saturday that authorizes an initial deployment of up to 300 unarmed military observers to Syria for three months to monitor a fragile week-old ceasefire in a 13-month old conflict. REUTERS/Allison Joyce (UNITED STATES - Tags: POLITICS)
UN-Sicherheitsrat tritt zur Verabschiedung einer Syrien-Resolution zusammenHoto: Reuters

Komitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ya kaɗa ƙuri'ar amincewa da matakin soji a arewacin Mali domin ƙwato yankin da ya faɗa a hannun ƙungiyoyin kishin islaman da suka haɗa da Ansar Dine da Mujao da kuma Aqmi wato Alqa'ida a yankin Maghreb. Dama tun can baya an samu rashin jittuwa tsakanin membobin komitin, musamman Faransa da Amurka a kan batun.
To saidai ko yanzu akwai sauran lokaci, inji wani jami'in diplomasiya,wanda ya ce ko da rundunar ta ECOWAS za ta fara aikinta na 'yantar da yankin sai da nan zuwa watan Satumban shekara ta 2013. Ita dai ECOWAS ta ce sojojinta da suka kai kimanin 3.300,na cikin shirin ko-ta-kwana ga isa yankin na arewacin Mali.
A nashi ɓangare, sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-Moon,ya ce babu dole sai rai ya so ga ƙasashen duniya a gudunmuwar da za su iya badawa a maimakon a ce Majalisar Dinkin Duniya ce zata ɗauki ɗawainiyar dakarun.

Mawallafi: Issuhu Maman
Edita: Yahouza Sadissou Madobi