1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Makomar Boko Haram bayan karbe Sambisa

December 29, 2016

Makomar mayakan kungiyar Boko Haram na ci gaba da daukar hankali a Najeriya da kasashen da ke makwabtaka da ita kwanaki kalilan bayan da rundunar soji ta sanar da kame dajin Sambisa .

https://p.dw.com/p/2V0Wb
Karikatur: Nigeria - Armee erobert Boko Haram Hochburg Sambisa
Hoto: DW

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sanar da cewar dakarun kasar sun karbe iko da babbar tungar 'yan Boko Haram da ke dajin Sambisa a jihar Borno, inda aka kame da dama a cikinsu. Tuni ma wasu mayakan Kungiyar Boko Haram suka mika wuya ga hukumomin Jihar Diffa ta Jamhuriyar Nijar.