1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali ta kama wasu 'yan ta'adda kimanin 20

Gazali Abdu TasawaJuly 15, 2015

Daga cikin 'yan ta'addar har da wasu Faransawa biyu da kuma wani mutun da ake zargi da kitsa harin da aka kai a watan Maris a wani gidan cin abinci na birnin Bamako.

https://p.dw.com/p/1Fyhr
Mali Anschlag auf ein Restaurant in Bamako
Hoto: AFP/Getty Images/H. Kouyate

Hukumomin 'yan sandar kasar Mali sun bada sanarwar kama wasu mutane kimanin 20 da su ke zargi da kasance wa 'yan jihadi, ciki har da wasu Faransawa biyu da kuma wani mai suna Saouty Kouma da dama suke neman ruwa a jallo a bisa zarginsa da kitsa wani harin ta'addanci da aka kai ranar bakwai ga watan Maris a wani gidan cin abinci na birnin Bamako, da ya yi sanadiyyar mutuwar wani dan kasar Faransa guda da kuma wani dan kasar Beljiyam.

Hukumomin tsaron kasar Malin sun ce sun damke mutuman ne a ranar lahadin da ta gabata a garin Melo da ke a tsakiyar kasar ta Mali a yayin da sauran mutanan wadanda akasarinsu 'yan asalin kasar Moritaniya ne sun kama su ne a ran Litanin a garin Zegoua da ke a kudancin kasar ta Mali. Kuma tuni suka iza keyarsu zuwa birnin Bamako domin yi musu tambayoyi.