1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta yi gargadi ga masu zanga-zanga

October 5, 2013

Mahukuntan Masar sun gargadi al'ummar kasar da suka daura aniyar yin zanga-zanga a kasar a ranar Lahadi da su guji yin hakan ko su fuskanci fushin hukuma.

https://p.dw.com/p/19uFX
Jordanians and Palestinians chant slogans and wave Muslim Brotherhood flags during a demonstration in the Jordanian capital Amman against Israel's deadly assault on the Gaza Strip March 2, 2008. More than 5,000 demonstrators marched peacefully from the headquarters of the Islamist-dominated trade unions to the parliament building in the city centre to protest Israel's deadly assault on the Hamas-run Gaza Strip. AFP PHOTO/AWAD AWAD (Photo credit should read AWAD AWAD/AFP/Getty Images)
Masu zanga-zanga a birnin Alkahiran MasarHoto: Awad Awad/AFP/Getty Images

Mai magana da yawun fadar mulkin kasar Ahmed al-Muslimani ne ya bayyana hakan a wannan Asabar din, kwana guda kafin cika shekaru arba'in da samun nasarar da Masar ta yi kan wani hari da suka kai wa sojin Isra'ila a wani yaki da suka gwabza.

Mr. al-Muslimani ya ce dukannin wanda ya yi kunnen kashi game da wannan gargadi da gwamnatin kasar mai samun goyon bayan soji ta yi, to shakka babu za su dauke shi a matsayin wanda wasu kasashen ketare ke mara wa baya wajen tada zaune a Masar.

Wannan sanarwar na zuwa ne daidai lokacin da 'yan jam'iyyar 'yan Uwa Musulmi ta hambararren shugaba Muhammad Mursi suka lashi takobin bazama kan tituna a wannan Lahadi domin nuna fushinsu ga sojin kasar wanda suka hambarar da gwamnatin Mursi watannin da suka gabata.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammad Nasiru Awal