1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Tattalin arziki

Najeriya: Shirin Fadama ya rage yunwa a Bauchi

Muhammad Waziri Aliyu
October 16, 2018

16 ga watan Oktoba, rana ce da Majalisar Dinkin Duniya ta kebe domin nazarin wadatar abinci a duniya baki daya. Manufar wannan rana ta hada da yaki da yunwa. Jihar Bauchi da ke arewacin Najeriya an samu ci-gaba.

https://p.dw.com/p/36drt
Guinea-Bissau Reisfelder
Hoto: DW/B. Darame

Shirin Fadama, shiri ne da gwamnatin Jihar Bauchi ta bullo da shi da nufin samar da wadataccen abinci ga mutanen jihar kasancewar a baya akwai tsofaffin hanyoyi da ake amfani da su saboda samar da abinci wadanda a yanzu kuma zamani ya chanja wanda hakan ke nufin neman wasu sababbin hanyoyin samar da abinci. Wannan na daga cikin dalilan samar da wannan shirin a jihar inda tuni ya yi nisa har ya kai ga mataki na uku.

Bangladesch Faridpur Juteproduction
Hoto: DW/Muhammad Mostafigur Rahman

Tuni dai jama'a musamman manoma suka rungumi wannan shiri na Fadama inda kuma zuwa yanzu za a iya cewa kwalliya ta biya kudin sabulu ta fuskar samun abinci a wadace a jihar sabanin yadda a baya jama'ar jihar ta Bauchi suke fama da karancin abinci kamar yadda Hassan Jibrin Rimi wani manomin rani wanda ya samu cin gajiyar shirin ya shaida mana.

Taken bikin ranar abinci ta duniyar a bana dai shi ne kawar da yunwa a tsakanin al'umma wanda kuma na daga cikin manufar hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya a shekara ta 2030, hukumar tana fatan ganin an fatattaki yunwa a tsakanin al'umma musamman marasa karfi.