1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matashi wanda ke hada na'urar samar da lantarki a Najeriya

Nasir Salisu ZangoSeptember 14, 2016

Ahmad Muhammad Sani matashi ne da ya ke hada na’urar samar da wutar lantarki ta hasken rana a unguwar Sharada da ke A Kano,kuma bayan haka yakan kirkiri na’urar kyankyasar kaji,tare da koyar da matasa sana'ar.

https://p.dw.com/p/1K1tk
Afrika Rwamagana Solar Farm in Ruanda
Hoto: Imago/Nature Picture Library

La'akari da yawaitar matasa masu zaman banza da kuma irin tarin hadarinsu,a cikin al'umma shi ne makasudin karfafa gwiwar matashin Ahmad Muhd sani,wanda Allah ya bude masa basirar kere-kere ya kuma yi amfani da ita wajen kyautata rayuwar 'yan uwansa matasa.Ahmad ya dai samu wannan fusaha ce a Dubai a lokacin da ya yi zama a can kuma a yanzu ya kan koyar da ita ga matasa a Najeriya.

Wani abu mai karin armashi shi ne furucin shi Ahmad Sani da ya ce hatta jami'ar Bayero ta Kano da makarantun fasaha mallakar gwamnatin Kano suna kawo masa dalibai domin samun ilimi,duk da cewar bai taba samun wani tagomashi koda na godiyya ba daga wata hukuma ta gwamnati.