1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsayin Afirka Ta Kudu a rikicin Afirka Ta Tsakiya

April 4, 2013

Afirka Ta Kudu ta ce za ta janye dakarunta daga jamhuriyyar Afirka Ta Tsakiya, bayan asarar sojojin da ta yi.

https://p.dw.com/p/189it
South African soldiers attend a memorial service for the South African soldiers who died during a battle with rebels in the Central African Republic at the Swartzkop Air Force Base in Pretoria on April 2, 2013.The thirteen soldiers were killed on March 23, 2013 on the outskirts of Bangui, twenty seven others were wounded. South African President Jacob Zuma who is facing anger at home dismissed claims that South African troops deployed in restive Central Africa were protecting private business interests as 'conspiracy theories.' AFP PHOTO / STEPHANE DE SAKUTIN (Photo credit should read STEPHANE DE SAKUTIN/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

Shugaban kasar Afirka Ta Kudu Jacob Zuma ya sanar da cewar, kasarsa za ta janye daukacin dakarunta daga jamhuriyyar Afirka Ta Tsakiya, bayan dakarunta 13 sun mutu yayin fito na fito da 'yan tawayen da suka yi nasarar kifar da gwamnatin shugaba Farancoir Bozize. Shugaban ya dauki wannan matakin ne, bayan sukar da yake ta sha dangane da asarar dakarun da kasar ta yi, wanda ke zama mafi yawa - a lokaci guda, tun bayan kawo karshen mulkin wariyar launin fata a kasar ta Afirka Ta Kudu.

Idan za'a iya tunawa dai akalla dakaru 13 ne suka mutu, yayin da wasu 27 kuma suka sami rauni a ranar 23 ga watan Maris daya gabata, sa'ilin da 'yan tawayen Seleka da yawansu yakai mayaka dubu ukku suka isa kusa da Bangui, babban birnin jamhuriyyar Afirka Ta Tsakiya, inda daga baya kuma suka yi nasarar kifar da gwamnatin da ke mulki a kasar.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mohammad Nasir Awal