1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsayin gwamnatin Mali a shari'ar Sanogo

December 2, 2013

Ma'aikatar tsaron Mali ta ce ba za ta yi katsalanda ko kuma yin kafar ungulu ga shari'ar da za a yi wa tsohon shugaban mulkin sojin kasar Janar Amadou Sanogo ba.

https://p.dw.com/p/1AS01
Mali's junta leader Amadou Haya Sanogo poses for a picture after agreeing to hand over power to the president of the National Assembly at his office at a military base in Kati in this April 7, 2012 file photo. When former colonial power France sent warplanes and troops to Mali on January 11, 2013 in a historic intervention, it did not just halt a menacing advance on the capital Bamako by Islamist rebels allied to al Qaeda. It also snuffed out what diplomats and local politicians say was a political conspiracy in the capital to oust Mali's interim civilian rulers, an attempted replay of the March 2012 coup that had plunged the Sahel state into turmoil and made it a potential launch pad for attacks on Western interests. To match Insight MALI-RECONSTRUCTION/ REUTERS/Joe Penney (MALI - Tags: POLITICS PROFILE CIVIL UNREST CONFLICT MILITARY)
Janar Amadou SanogoHoto: Reuters

Ma'aikatar tsaron Mali ta ce ba za ta yi katsalanda ko kuma yin kafar ungulu ga shari'ar da za a yi wa tsohon shugaban mulkin sojin kasar Janar Amadou Sanogo ba.

Ministan tsaron na kasar Soumeylou Boubeye Maiga ne ya bayyana hakan a yau, inda ya ce zai tabbata ya bada tallafi don shari'ar ta gudana ba tare da wata matsala ba, kana ce zai kokarin ganin duk sojan da aka gayyata ya bada ba'asi ya je kotun don yin hakan.

Mr. Maiga ya kuma ce gwamnatin kasar ba ta da hannu wajen tsare Janar Sonogo da aka yi da ma dai gurfanarsa gaban kuliya, mutanen da aka yi wa ba daidai ba lokacin da Sonogon ke kan mulki ne suka nemi kotu ta bi musu kadi.

Ana dai tuhumar Janar Amadou Sonogo ne da bacewar wani hafsan sojin kasar da ma dai mutuwar wasu soji shidda lokacin wani bore da sojoji suka sa'ilin da ya ke jagogarantar kasar bayan juyin mulkin da ya yi cikin watan Maris din shekara ta 2012.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Pinado Abdu-Waba