1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD: Ta ce kisan Rohingyas da gangan ne.

Abdourahamane Hassane
October 11, 2017

Sakamakon wani bincike da kwararru na MDD suka kaddamar ya nuna cewar kisan da aka rika yi wa 'yan kabilar Rohingyas na kasar Bama da gangan ne.

https://p.dw.com/p/2lduq
Bangladesch Rohingyas im Flüchtlingslager Cox's Bazar
Hoto: Reuters/M.P. Hossain

Rahoton na Majalisar Dinkin Duniya ya ce kisan wani abu ne da aka tsara da nufin kawar da tsirarun kabilun Musulmi na Rohingyas baki daya daga kasar ta Bama. Masu yin binciken sun yi tambayoyi ga gomai na jama'ar da suka tsere daga yankin Rakhine zuwa Bangladesh bayan barkewar tashin hankalin a cikin watan Augustan da  ya gabata