1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bukatar kaddamar da bincike a Burundi

Abdourahamane Hassane
July 14, 2020

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira ga sabuwar gwamnati Burundi da ta kawo karshen tashin hankalin da ake fama da shi a kasar.

https://p.dw.com/p/3fJ4F
Neuer Präsident von Burundi, Evariste Ndayishimiye
Hoto: DW/A. Niragira

A cikin wata sanarwa da kwamitin bincike na MDD a kan Burundi ya bayyana ya bukaci sabon shugaban na Burundi Évariste Ndayishimiye ba da hadin kai wajen sake bude cibiyar kare hakin dan Adam ta majalisar a Burundi.Tun a shekara ta 2016 kwamitin kare hakin dan Adam na MDD ya soma gudanar da bincike a kan tafka ta'asa a Burundin. Tashin hankali biyo bayan zaben da aka yi a shekara ta 2015 mutane dubu 12 suka mutu, yayin da wasu dubu 400 suka yi kaura daga kasar.