1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD: 'Yan hijira sun karu a duniya

November 3, 2017

Majalisar Dinkin Duniya ta ce masu zaman hijira a duniya sun yi matukar karuwa a shekaru takwas din da suka gabata, daga mutum miliyan 42 zuwa mutum miliyan 66.

https://p.dw.com/p/2myR2
Südsudan UNAMIS Camp Juba 22.12.2013
Hoto: Tony karumba/AFP/Getty Images

Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, ta ce masu zaman hijira a duniya sun yi matukar karuwa a shekaru takwas din da suka gabata, daga mutum miliyan 42 zuwa mutum miliyan 66. A cewar hukumar raguwar kokarin al'umar duniya na rage ko kuma sasanta rigingimu ne ke zama musabbabin ta'azzarar wannan lamari.

Wani babban jami'i a hukumar Filippo Grandi, shi ne ya shaida wa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya hakan a birnin New Yorka na Amirka. Kuma kasashen Syria da Iraki kadai sun kwashi kaso mafi yawa na wadanda suka bar muhallansu a duniyar yau. Na baya-bayan nan kuwa su ne wasu musulmi marasa rinjaye 'yan Rohingya na kasar Bama su dubu 500 da rikici ya raba da sukuni inda a halin yanzu suke fakewa a kasar Bagaladash.