1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Pompeo da Merkel za su gana kan batutwa da dama

Abdoulaye Mamane Amadou
November 1, 2019

Fadar gwamnatin Jamus ta bayyana cewa sakataren harkokin wajen Amirka Mike Pompeo zai kaddamar da wata ziyarar aiki a birnin Berlin, inda zai gana da shugabar gwamnatin kasar Angela Merkel da sauran kusoshin gwamnati.

https://p.dw.com/p/3SM4E
Deutschland Berlin | US Außenminister Mike Pompeo auf Staatsbesuch mi Angela Merkel
Hoto: Reuters/F. Bensch

Duk da yake sanarwar fadar gwamnatin ba ta fito fili ta fayyacce ko batun girka rundunar hadin gwiwa ta sojan kasa da kasa a arewacin Siriya na daga ciki jadawalin tattaunawar da za ta shiga tsakanin Pompeo da Merkel ba.

Rahotanni sun ce Sakatare Pompeo zai gana da wasu kusoshin gwamnatin Jamus ciki har da sakataren harkokin wajen Jamus Heiko Maas da ministar tsaro Annegret Kramp-Karrenbauer.