1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ministocin tsaron kasashen Jamus da Mongoliya sun gana

Zulaiha Abubakar
October 20, 2018

Ministar tsaron Tararayyar Jamus Ursula von der Leyen ta fara ziyarar aiki a kasashen Asia da Ostiriliya da kuma Mongoliya don neman hadin kan Sojoji don yaki da ayyukan ta'adda ta kafar Internet. .

https://p.dw.com/p/36sh6
Mongolei Besuch Ursula von der Leyen | Treffen mit mongolischen Soldatinnen
Hoto: DW/M. Koschyk

Tun da fari Ministar ta gana da takwaranta na Mongoliya da kuma mataimakin Firaministan kasar bayan ta ziyarci wani sansani da Sojojin Jamus suke horas da Jami'an tsaron Mongoliya wadanda ke aikin tsaro a Afghnistan, dama dai Sojojin kasashen biyu na wani aikin hadin gwiwa a Afghanistan tare da dakarun rundunar tsaron Majalisar Dinkin Duniya.

A gobe Lahadi Ministar tsaron za ta ziyarci kasar Chaina don tattaunawa da shugabannin bangarorin tsaro a kasar.