1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mugabe ya nemi a bashi kariya a Zimbabuwe

Yusuf Bala Nayaya
November 23, 2017

Majiya daga bangaren gwamnatin Zimbabuwe ta bayyana cewa Mugabe dan shekaru 93 ya fadawa masu shiga tsakanin cewa ya na so ya mutu a kasar ta Zimbabuwe ba shi da wani buri na barin kasar don neman mafakar siyasa.

https://p.dw.com/p/2o8Q9
Simbabwe Mugabe bei TV-Ansprache
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Tsohon shugaban kasar Zimbabuwe Robert Mugabe ya samu tabbaci na cewa ba za a gurfanar da shi gaban kuliya ba kuma zai samu tsaro na lafiyarsa a kasarsa ta haihuwa a wani bangare na yarjejeniyar da aka kulla da shi kafin ya mika takardar ajiye mukamin shugabancin kasar kamar yadda wata majiya da ke kusa da wadanda suka shirya yarjejeniyar ta nunar a wannan rana ta Alhamis.

Majiyar daga bangaren gwamnatin Zimbabuwe ta bayyana cewa Mugabe dan shekaru 93 ya fadawa masu shiga tsakanin cewa ya na so ya mutu a kasar ta Zimbabuwe ba shi da wani buri na barin kasar don neman mafakar siyasa.

A cewar majiyar da ba ta so a bayyanata ba, Mugabe ya yi jawabin nasa a yanayi na kada zuciya kuma ya ce daukar matakin ya zame masa dole ne. A gobe Juma'a ne dai ake sa ran za a rantsar da Emmerson Mnangagwa mataimaki da Mugabe ya kora da kuma ya koma gida a ranar Laraba.