1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Musulmai sun shirya gangami a Jamus

January 13, 2015

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta shirya shiga wannan gangami da al'ummar Musulmi suka shirya a yau Talata don nuna muhimmancin zaman tare.

https://p.dw.com/p/1EJGR
Aktionstag der deutschen Muslime 19.9.2014 Muslime gegen Hass
Hoto: Reuters/Hannibal

A yayin wannan gangami Musulman zasu nuna adawa da shirin kai farmaki da aka kai wa wasu ma'aikatan mujalla a birnin Paris sannan su mika sako ga dubban masu adawa da yawaitar Musulmi a kasar.

Shugaba Joachim Gauck na kasar ta Jamus zai yi jawabi ga taron da misalin karfe biyar na yammaci agogon kasar a birnin Berlin gaban katafariyar kofar nan mai tarihi ta Brandenburg.

Wannan gangami dai cibiyar mabiya addinnin na Islama da ke a nan Jamus ta shirya shi wanda aka yi masa lakabin "Mu zauna da juna dan taimakon kanmu ta'addanci ba da sunanmuba" .

Da yawa cikin mambobin majalisar zartarwar shugaba Markel zasu mara mata baya a wajen wannan gangami dan nuna adawa da masu nuna wa Musulmin kyama daga kungiyar Pegida, inda ta jaddada a jiya Litinin cewa Musulunci wani bangare ne na Jamus.

A jiya dai wadanda suka shiga macin kungiyar ta Pegida sun kai 25,000 a gangamin da suka yi karo na 12 a birnin Dresden.

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Umaru Aliyu