1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 17 sun rasu a tashin hankali a arewacin Najeriya

April 29, 2013

Rahotanni daga garin Bama dake jihar Borno sun ce wata musayar wuta da aka yi tsakanin jami'an tsaro da 'yan bindiga ta yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

https://p.dw.com/p/18PGR
Soldier patrol to monitor protesters at Ojota district in Lagos on January 16, 2012. Nigerian security forces fired tear gas and shot into the air Monday to disperse around 300 protesters in Lagos as authorities moved to prevent demonstrations in various parts of the country. Nigerian unions announced on January 16 they were suspending a week-old nationwide strike over fuel prices which has shut down Africa's most populous nation and brought tens of thousands out in protest. AFP PHOTO/PIUS UTOMI EKPEI (Photo credit should read PIUS UTOMI EKPEI/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/AFP

Wani jami'in soji a tarayyar Najeriya ya ce an halaka akalla mutane 17 a wani fada da aka gwabza tsakanin 'yan bindiga da dakarun tsaro a yankin arewa maso gabacin tarayyar ta Najeriya. An gwabza fadan ne a garin Bama dake a jihar Borno, inda tun a shekarar 2010 'yan bindiga ke fafatawa da dakarun gwamnati. Laftanan Kanal A.G. Laka ya fada a wannan Litinin cewa fadan yayi sanadiyar mutuwar jami'an 'yan sanda bakwai da kuma 'yan bindiga 10. 'Yan jarida da ke wa wata tawagar gwamnati rakiya a yankin sun ce ba su ga gawa ko guda daya ba, sai dai sau da yawa sojoji a Najeriya na rage yawan wadanda irin wannan tashin hankali kan rutsa da su. Wani dan jarida ya ce an kona gidaje da kuma shaguna da kuma wuraren kasuwanci.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Zainab Mohammed Abubakar