1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 20 sun mutu a wani hari a Iraki

July 19, 2013

Wani dan harin kunar bakin wake ya tada bam a wani masallacin mabiya tafarkin Sunnah a birnin Bagadazan kasar Iraki, inda hakan ya yi sanadiyyar rasuwar mutane ashirin.

https://p.dw.com/p/19Apo
Iraqi security forces inspect the site of a car bomb attack in Kirkuk, 250 km (155 miles) north of Baghdad, July 11, 2013. Two civilians were wounded after the car bomb attack, police said. REUTERS/Ako Rasheed (IRAQ - Tags: CIVIL UNREST POLITICS)
Anschlag Irak KirkukHoto: Reuters

Jami'an 'yan sanda da ke Bakuba a birnin na Bagadazan wanda su ka tabbatar da kai harin sun ce baya ga asarar rayukan da aka samu a harin, wasu mutane arba'in sun jikkata.

Yankin na Bakuba da aka kai wannan hari na yau dai ya sha fama da hare-hare irin wadannan domin ko a ranar Talatar da ta gabata sai da aka kai hari kan mabiya tafarkin na Sunna a wani masallaci da ke Muqdadiyah inda mutane sha biyar su ka ce ga garinku nan.

Kawo yanzu dai babu wata kungiya da ta dau alhakin kai harin na yau, sai dai hukumomi sun ce su na ta yin bakin kokarinsu wajen bankado wadanda ke da hannu domin gurfanar da su gaban kuliya.

Mawallafi. Ahmed Salisu
Edita: Mohammed Awal Balarabe