1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane aƙalla 26 ne suka rasu a hare-hare a Iraƙi

October 16, 2014

Hare-haren 'yan Ƙungiyar IS a IraƘi sun yi sanadiyyar rasuwar mutane 26 a wannan Alhamis ɗin, yayin da wasu da dama suka jikkata, a birnin Bagadaza da kuma Mahmoudiyah.

https://p.dw.com/p/1DWkE
Bombenanschlag in Bagdad Irak 11.10.2014
Hoto: REUTERS/T. Al-Sudani

Da farko dai wasu motoci ne biyu shake da bama-bamai suka tarwatse a Kazimiya da ke arewa maso yammacin birnin Bagadaza inda mutane 10 suka rasu tare da jikkata wasu 29, sannan wani ɗan ƙunar bakin wake ya tarwatsa motar sa a unguwar Talibiya cikin birnin na Bagadaza inda nan ma mutane tara suka rasu wasu kuma 26 suka jikkata, sai kuma a Mahmoudiyah da ke a nisan km 30 a kudancin binin na Bagadaza inda mutane aƙalla bakoye suka rasu.

A cewar Majalisar Ɗinkin Duniya aƙalla mutane 1100 ne suka mutu sakamakon hare-haren ta'addanci a ƙasar ta Iraƙi a watan Satumba da ya gabata, inda daga farkon watan nan na Oktoba kawo yanzu aƙalla wasu mutane 400 sun rasu sakamakon hare-haren.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Abdourahmane Hassane