1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutum na takwas ya kamu da Ebola a Mali

Abdourahamane HassaneNovember 25, 2014

Gwamnatin ta Mali ta ce ta killace mutumin sannan kuma ta ce tana sa ido a kan wasu mutane 271 waɗanda suka yi mu'ammula da mutumin.

https://p.dw.com/p/1DsXf
Mali Kourémalé Ebola
Hoto: DW/J.-P. Scholz

Hukumomin kiwon lafiya a ƙasar Mali sun ba da sanarwar cewar an samu mutum na takwas da ya kamu da cutar Ebola a ƙasar. Tun da farko a ranar Asabar da ta gabata ofishin ministan kiwon lafiya na ƙasar ya sanar da cewar an samu ƙarin wani mutumin da ya kamu da cutar.

Gwamnatin ƙasar ta Mali ta ce an killace mutanen a wata cibiya ,ana jinyarsu sannan kuma ta ce ana sa ido a kan wasu mutane 271 da suka yi cuɗanya da waɗanda ake jinyar.