1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Za a yi zabe da na'urar tantance kuri'a

Uwais Abubakar Idris AH
December 11, 2018

Hukumar zaben Najeriya ta ba da tabbacin cewar za ta yi amfani da nau'rar tatance katin masu jefa kuri’a a zabe na 2019, amma fa babu batun tattara sakamakon ta hanyar yanar gizo.

https://p.dw.com/p/39tPB
Wahl Nigeria Abuja
Hoto: DW/Uwaisu A. Idris

Tabbacin da hukumar zaben Najeriyar ta bayar dai ya kara kwantar da hankalin ‘yan Najeriya da dama a game da sanin inda aka kwana a zaben na badi, musamman biyo bayan rashin sanya hannu a dokar zaben kasar da aka yi wa gyaran fuska, wacce a cikinta ne dukkanin wasu sauye-sauye da ma samun hallaci na doka ke ciki. 

Nigeria, Wählerin mit Wählerkarte
Hoto: AFP/Getty Images/P. Utomi Ekpei

Ko da yake ga jam'iyyun adawa na masu dagewa a kan samun dokar zaben ta Najeriya da za ta hallata tattara sakamakon zaben ta hanyar nau'ra mai aiki da kwakwalwa, amma wane tasiri samun haske da tabbaci daga hukumar zabe a kan amfani da katin zai yi dama hallacin hakan. Wani abin da ya fi daukan hankali shi ne yanke shawarar da hukumar zaben ta yi a zaben na badi na cewar ba za’a sake amfani da takardar kadara ba, wacce a kan cika idan nau'ra ta kasa tatance katin jefa kuri’a. A yayin da ake ci gaba da cece-kuce a kan shirye-shiryen zaben na Najeriya da aka sanyawa hukumar zaben ido sosai, amfani da iko na tsara zaben da doka ta bai wa hukumar muhimmi ne a kokuwar da ake na inganta sahihanci zaben fiye da na shekara ta 2015, don kaucewa ci gaba irin na mai ginan rijiya.