1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: An saki daruruwan 'yan Boko Haram

Ramatu Garba Baba
February 18, 2018

Hukumomi a Najeriya sun sanar da sakin wasu mutane 475 da aka kama bisa zarginsu da zama mambobin kungiyar Boko Haram bayan da aka gagara samun shaidu da za su tabbatar da zargin da ake musu.

https://p.dw.com/p/2stsN
Boko Haram
Hoto: Java

Mutanen dari hudu da saba'in da bakwai na daga cikin mambobin kungiyar dubu daya da aka soma yi wa shari'a a makon jiya a garin Kainji da ke a jahar Naija.

Salihu Othman Isah, wani mai bai wa Atoni Janar na kasar shawara ne ya sanar da sakin mambobin, ya kara da cewa daukar matakin ya zama wajibi bayan da aka gaggara samun gamsassun sheda dake tabbatar da zargin da ake musu na tallafawa ayyukan kungiyar ko kin bayar da bayanai da za su taimakawa masu bincike kan ayyukan kungiyar ba.

Yanzu  za'a aika da mutanen jihohinsu inda za a yi ta basu shawarwari kan yadda za su ci gaba da rayuwa cikin sauran al'umma. Shugaban Najeriyan Muhammadu Buhari a baya-bayan nan ya yi ikirarin kawo karshen kungiyar da ta yi sanadiyar rayukan dubban mutane a sanadiyar hare-haren bama bamai.